Tabaraka Allah mai iko,
Ranar da ba wani mai iko,
Mamallakin ran sakamako,
Kayi mu d'ai ba fifiko,
Nufinka ne Jalla Rabbana.
Wakar ga ta sa ni zulumi,
Ina ta tunani nai tagumi,
Na ji ta ni tun ina karami,
Ban manta ba cikin azumi
Isma'eel ke wakar damina
Shukuran ba na fahari,
Ni zuciyata duk tai fari,
Ina ta zogi ina marari,
Ina ta zumudin yin k'ari,
Acikin wakarnan ta damina.
'Yan baitukana babu yawa,
Wai motsi ya fi labewa,
Koda kana can cikin dawa,
Ga Zaki da Kura ga Giwa,
Tsiranka sai dai Jalla Rabbana.
Lallai an sha ruwan fari,
Duk Zuciyarmu tayi fari,
Albarka mai kauda fari,
Jalla kawar da dodon fari,
Ma su cinye amfani da damina.
Ga gaisuwa ta ga Na'ibi,
Nayi tane cikin ladabi,
Shafa ni na bar tararrabi,
Nayi rubutu babi-babi,
Rabbi kai nake wa rokona.
Anan nake so ni zan tsaya,
Mai ta'aliki ba gajiya,
BNG mai karafkiya,
Lalube nake neman hanya,
Acikin duhun daren damina.
Monday, July 9, 2007
Saturday, July 7, 2007
Wak'ar Damina. Malam Na'ibi Sulaimanu Wali
Bismilla Allah Madawwami,
Shi Mahaliccinmu Rahimi,
Mai yawaita alheri magami,
Wanda ya yi rani da damina.
Komai yana yi mai ma'ana,
Don hikimominsa Rabbana,
Masu yawa ko a ko ina,
Tabaraka Sarkin sarakuna,
Ya sa ni'imomi ga damina.
Nomau manomi mai dariya,
Tsaya inai maka tambaya,
Shin me yake ba ka dariya,
Ko kana da jikkar zinariya,
Ko ko ka ci riba da damina.
Sai ya kada baki da hamzari,
Ya ce da ni kai albishiri,
Yau zuciyata ta yi fari,
Zak'inta ya zarce sukari,
Na ga malama ta damina.
D'ago kai ka dubo samaniya,
Ka ga gajimarai na tafiya,
Kafin na bushe da dariya,
Sai na ji tsawa da walkiya,
Suna bushara ga damina.
Nan da nan gari ya fitittike,
Kamar girar sa a murtuke,
Wanda aka d'aure jikin turke,
To nan da nan sai mun ka fake,
Don gudun jik'ewa ga damina.
Sai cida ka ke ji cikin gari,
Sama tayi damkam sai hadari,
Tafiya yake yi da hanzari,
Kamar ana kora ayari,
Hauragiya sai su damina.
In ka ga haske da walkiya,
Kamar wutar Yola tunniya,
Sararin sama na rugunniya,
Kamar maza na hayaniya,
Nam'an wa haufan ga damina.
Za ka ga iska da guguwa,
Suna ta shara da kokawa,
Suna busharar akwai ruwa,
Kowa ya shirya yana zuwa,
Mu ne ma'aikata na damina.
Ku masu shanya ku tattara,
Ko ku masu murhu ku ciccira,
Kafin ka ce ga bakin zare,
Sai ruwa ya tsuge cikin dare,
Ya nuna halinta damina.
Ruwa ya kwana guna-guna,
Kamar ana yi da guguna,
Sai kankara ga ta ko ana,
Allah jikan wasu d'akuna,
Yau damina ta yi damina.
Abin sha'awa sai da jijjifi,
Ko ana ka duba kamar afi,
Ka ga mutane ba lissafi,
Gonarsa kowa yakan tafi,
Da iri ya shuka da damina.
Kan a jima ko a ko'ana,
Gud'a ka ke ji da ganguna,
Yau fa manoma kamar dina,
Sai jefa garma da jinina,
Ayyuriri mu na damina.
Kwana kadan kungi yawuwa,
Gyada da dawa da yakuwa,
Duk sun yi kore gwanin k'awa,
Dukan yabanya sai yad'uwa,
Saboda danshi na damina.
Sai kurum a ran nan da safiya,
Nomau ya b'ullo da dariya,
Ya ce dani za shi gewaya,
Nan take sai muka rankaya,
Muna bushara ga damina.
Dawa da gero sai rangwad'a,
Kamar amare gidan kid'a,
Sannan da dubo wajen gyad'a,
Sai na ganta shar-shar tana fad'a,
Na gode aikinki damina.
Daga nan na jiya ga auduga,
Duk inda na hango ta sai na ga,
Sai dariya ba k'ididdiga,
Kai, fara'a sai su auduga,
Saboda tsarinta damina.
Sai muka koma da murmushi,
Ya bud'e baki da dasashi,
Kamar da d'ai ba shi yin fushi,
Yana fad'in "duk mai karfi"
Za ya sami kud'i da damina.
Ran da za'a girbi kamar buki,
Kowa da lauje suke jiki,
Kan a jima babu ko haki,
An daure damai daki-daki,
Ka ji hukuncinta damina.
Kai a takaice in ce da kai,
Sai na ga jakai akai akai,
Suna jido sai su zo su kai,
Buhu da dammai har masakai,
Albarkaci ne na damina,
Kaka uwa ce ga damina,
Idan ta bullo a ko ina,
Za ka ga manya da kankana,
Suna ta harka da kunbuna,
Saboda innarmu damina.
Tun daga k'auye ka ke gani,
Kowa ne babba da kankani,
Harkarsu sai wanda ya sani,
Mata ko sai kirma a zani,
Saboda kaka ta damina.
Haukan su nomau na dayawa,
Wai sun ga kudi na samuwa,
Aure suke yi babu haihuwa,
A kai a kai ka yi faduwa,
Da watsa ni'ima ta damina.
Manyan samari da kankana,
Sai taguwoyi da riguna,
Ga jakuna nan da dokuna,
Wasunsu har ma da kekuna,
Bore suke yi wa damina.
Nan na ga shanu na ta dara,
Ywansu wane d'ari tara,
Sun yi k'iba duk ga madara,
Sun sami d'anya suna ta cira,
Sun ci harawa ta damina.
Kai a tak'aice ko ka jiya,
Komai ka duba ko bishiya,
Za ka ga ta sake rausaya,
Kamar amarya ko gimbiya,
kowa gada ta sa damina.
Kai direba mai giwa a dawa,
Ina ka b'ullo na zuwa,
Ko lafiya Sarkin sukuwa?
Na ga gudun naka yai yawa,
Ga sh kuwa mun zarce damina.
Sai ya ce da ni hanga ka gani,
Ka san sukuwa sai mutum gwani,
Shi dai ya ka yi ba ya lahani,
Dalar gyada an kace da ni,
Nai ta jido wa da damina.
Daga zuwa na cikin gari,
Sai k'ungiyoyi d'ari-d'ari,
Suna ta aiki da hamzari,
Wassu suna kan basukuri,
Albarkacin gwaggo damina.
Idan duk ka duba a ko ana,
Babur da mota da kekuna,
Kamar gafiyoyi a titina,
Su yi kasuwa su yi kantuna,
Kowa busy sai su damina.
Yaran gari ko sai bal suke,
Kowa ka duba very happy,
Da damina dai mutum take,
Da an mutum sai son a sake,
Ka ji suffofinta damina.
In da mutum ce ba garari,
Da an mutum mai halin gari,
Kogina baiwa ba had'ari,
Mai mai da dukkan bak'i fari,
Mai fara'a ka ji damina.
Mai dariya mai son shagali,
Ko ya yi fad'a wani sa'ili,
Sai ka ce da shi sannu adali,
Kyautarka ta zarce misali,
Allah ya bar mana damina.
Kaka uwar yalwatar gari,
Da mace ce za'ai ta gari,
Mai baiwa jikokinta d'ari,
Ta sha da su nonon sukari,
Kaka uwar inna damina.
Na gode Allah Ubangiji,
Wanda ya ba ni gani da ji,
Ya ba ni tunani aji-aji,
Tabaraka na rok'i agaji,
Ka ba ni hazzi da damina.
Mai tambaya in ka so ka bi,
Suna na yanka ko lak'abi
Ce Adamu ko ko Na'ibi,
Wali Sulaimanu ne Abi,
Wanda ya wawwak'e damina.
Alhamdulillahi a gama,
Na kama doki mai ragama,
Na yi tab'i na yi tak'ama,
Na sauka ba wata gardama,
Saboda kaka da damina.
Muna salati ga Annabi,
Muhammadu wanda mu ke ta bi,
Kazalika Alu da Sahhabi,
Da Auliya'u da masu bi,
Baiwarsu ta zarce damina.
Shi Mahaliccinmu Rahimi,
Mai yawaita alheri magami,
Wanda ya yi rani da damina.
Komai yana yi mai ma'ana,
Don hikimominsa Rabbana,
Masu yawa ko a ko ina,
Tabaraka Sarkin sarakuna,
Ya sa ni'imomi ga damina.
Nomau manomi mai dariya,
Tsaya inai maka tambaya,
Shin me yake ba ka dariya,
Ko kana da jikkar zinariya,
Ko ko ka ci riba da damina.
Sai ya kada baki da hamzari,
Ya ce da ni kai albishiri,
Yau zuciyata ta yi fari,
Zak'inta ya zarce sukari,
Na ga malama ta damina.
D'ago kai ka dubo samaniya,
Ka ga gajimarai na tafiya,
Kafin na bushe da dariya,
Sai na ji tsawa da walkiya,
Suna bushara ga damina.
Nan da nan gari ya fitittike,
Kamar girar sa a murtuke,
Wanda aka d'aure jikin turke,
To nan da nan sai mun ka fake,
Don gudun jik'ewa ga damina.
Sai cida ka ke ji cikin gari,
Sama tayi damkam sai hadari,
Tafiya yake yi da hanzari,
Kamar ana kora ayari,
Hauragiya sai su damina.
In ka ga haske da walkiya,
Kamar wutar Yola tunniya,
Sararin sama na rugunniya,
Kamar maza na hayaniya,
Nam'an wa haufan ga damina.
Za ka ga iska da guguwa,
Suna ta shara da kokawa,
Suna busharar akwai ruwa,
Kowa ya shirya yana zuwa,
Mu ne ma'aikata na damina.
Ku masu shanya ku tattara,
Ko ku masu murhu ku ciccira,
Kafin ka ce ga bakin zare,
Sai ruwa ya tsuge cikin dare,
Ya nuna halinta damina.
Ruwa ya kwana guna-guna,
Kamar ana yi da guguna,
Sai kankara ga ta ko ana,
Allah jikan wasu d'akuna,
Yau damina ta yi damina.
Abin sha'awa sai da jijjifi,
Ko ana ka duba kamar afi,
Ka ga mutane ba lissafi,
Gonarsa kowa yakan tafi,
Da iri ya shuka da damina.
Kan a jima ko a ko'ana,
Gud'a ka ke ji da ganguna,
Yau fa manoma kamar dina,
Sai jefa garma da jinina,
Ayyuriri mu na damina.
Kwana kadan kungi yawuwa,
Gyada da dawa da yakuwa,
Duk sun yi kore gwanin k'awa,
Dukan yabanya sai yad'uwa,
Saboda danshi na damina.
Sai kurum a ran nan da safiya,
Nomau ya b'ullo da dariya,
Ya ce dani za shi gewaya,
Nan take sai muka rankaya,
Muna bushara ga damina.
Dawa da gero sai rangwad'a,
Kamar amare gidan kid'a,
Sannan da dubo wajen gyad'a,
Sai na ganta shar-shar tana fad'a,
Na gode aikinki damina.
Daga nan na jiya ga auduga,
Duk inda na hango ta sai na ga,
Sai dariya ba k'ididdiga,
Kai, fara'a sai su auduga,
Saboda tsarinta damina.
Sai muka koma da murmushi,
Ya bud'e baki da dasashi,
Kamar da d'ai ba shi yin fushi,
Yana fad'in "duk mai karfi"
Za ya sami kud'i da damina.
Ran da za'a girbi kamar buki,
Kowa da lauje suke jiki,
Kan a jima babu ko haki,
An daure damai daki-daki,
Ka ji hukuncinta damina.
Kai a takaice in ce da kai,
Sai na ga jakai akai akai,
Suna jido sai su zo su kai,
Buhu da dammai har masakai,
Albarkaci ne na damina,
Kaka uwa ce ga damina,
Idan ta bullo a ko ina,
Za ka ga manya da kankana,
Suna ta harka da kunbuna,
Saboda innarmu damina.
Tun daga k'auye ka ke gani,
Kowa ne babba da kankani,
Harkarsu sai wanda ya sani,
Mata ko sai kirma a zani,
Saboda kaka ta damina.
Haukan su nomau na dayawa,
Wai sun ga kudi na samuwa,
Aure suke yi babu haihuwa,
A kai a kai ka yi faduwa,
Da watsa ni'ima ta damina.
Manyan samari da kankana,
Sai taguwoyi da riguna,
Ga jakuna nan da dokuna,
Wasunsu har ma da kekuna,
Bore suke yi wa damina.
Nan na ga shanu na ta dara,
Ywansu wane d'ari tara,
Sun yi k'iba duk ga madara,
Sun sami d'anya suna ta cira,
Sun ci harawa ta damina.
Kai a tak'aice ko ka jiya,
Komai ka duba ko bishiya,
Za ka ga ta sake rausaya,
Kamar amarya ko gimbiya,
kowa gada ta sa damina.
Kai direba mai giwa a dawa,
Ina ka b'ullo na zuwa,
Ko lafiya Sarkin sukuwa?
Na ga gudun naka yai yawa,
Ga sh kuwa mun zarce damina.
Sai ya ce da ni hanga ka gani,
Ka san sukuwa sai mutum gwani,
Shi dai ya ka yi ba ya lahani,
Dalar gyada an kace da ni,
Nai ta jido wa da damina.
Daga zuwa na cikin gari,
Sai k'ungiyoyi d'ari-d'ari,
Suna ta aiki da hamzari,
Wassu suna kan basukuri,
Albarkacin gwaggo damina.
Idan duk ka duba a ko ana,
Babur da mota da kekuna,
Kamar gafiyoyi a titina,
Su yi kasuwa su yi kantuna,
Kowa busy sai su damina.
Yaran gari ko sai bal suke,
Kowa ka duba very happy,
Da damina dai mutum take,
Da an mutum sai son a sake,
Ka ji suffofinta damina.
In da mutum ce ba garari,
Da an mutum mai halin gari,
Kogina baiwa ba had'ari,
Mai mai da dukkan bak'i fari,
Mai fara'a ka ji damina.
Mai dariya mai son shagali,
Ko ya yi fad'a wani sa'ili,
Sai ka ce da shi sannu adali,
Kyautarka ta zarce misali,
Allah ya bar mana damina.
Kaka uwar yalwatar gari,
Da mace ce za'ai ta gari,
Mai baiwa jikokinta d'ari,
Ta sha da su nonon sukari,
Kaka uwar inna damina.
Na gode Allah Ubangiji,
Wanda ya ba ni gani da ji,
Ya ba ni tunani aji-aji,
Tabaraka na rok'i agaji,
Ka ba ni hazzi da damina.
Mai tambaya in ka so ka bi,
Suna na yanka ko lak'abi
Ce Adamu ko ko Na'ibi,
Wali Sulaimanu ne Abi,
Wanda ya wawwak'e damina.
Alhamdulillahi a gama,
Na kama doki mai ragama,
Na yi tab'i na yi tak'ama,
Na sauka ba wata gardama,
Saboda kaka da damina.
Muna salati ga Annabi,
Muhammadu wanda mu ke ta bi,
Kazalika Alu da Sahhabi,
Da Auliya'u da masu bi,
Baiwarsu ta zarce damina.
Wednesday, July 4, 2007
Wakar Begen Muhammadu, ta Malam Nasiru Kabara.
Begen Muhammadu ya cikamini zuciya,
Acikinta ba sauran muhalli ko daya.
Wallahi garwashin bidarsa du da shi,
Ya k'ona sassan zuciya wayaniya.
Na so ka D'aha kamar ido ga makauniya,
Na so in je ni gare koda sau daya.
Na so ziyara ga ni ba ni da fuffuke,
K'ak'a ni kai in gano masoyin zuciya.
Na so ka san mai wabiya da ta so d'iya,
Koko muridhi yadda ya so lafiya.
Ko son abinci ga wanda ya yunwata,
Koko ruwa ga mai k'ishi da ya sha wuya.
Mukhtaru ka tafi ban ganka a duniya,
Ko na rabauta in ganka ko kun kwanciya.
Acikin mafarkin in na samu sai in ce,
Allahu Akbar u'uhu wayyoniya.
Begenka ya k'onan k'ashi har jijiya,
Naman jikina ya zagwanye bai d'aya.
Ya k'ona hanta har da hanji duka,
Ya bar hawayen zuciya da idaniya.
K'aunarka ta k'one buk'atar zuciya,
Sai ko ganinka da yammaci ko safiya.
Ta ya da zancen duniya tatsuniya
Ta dauki amri wanda ya zam gaskiya.
Ta ya da zancen zo-mu-ji-ta da kan fad'a,
Ta kalmashe gizo ta hana masa k'ok'iya.
Duka zuciyar da ta so ka D'aha da gaskiya,
Wallahi ta arzurta ba shauran tsiya.
Tai sitira ta tufata launi bam da bam,
La budda tai sha'ani irin na hawainiya.
Wata safiya tai murmushi wata safiya,
Riga fara wataran ta sawo shudiya.
Wataran da alkebba fara wataran ko,
Ya fashe da kuka ni a wa d'an saniya.
K'ak'a ni kai na bak'in cikin nan duniya,
Wa zan k'ara gunsa ne wayyo niya.
Ko na yi k'ara babu mai ji ko ya zam,
kukan amale ni ka yi ko jiniya.
Mukhtaru ya faku ga ganinsa yai wuya,
Belle in ce masa D'aha ni na sha wuya.
Shi ne abin k'ara gare shi gani na sa,
Ya zam kamar k'oyin farar hankakiya.
Acikinta ba sauran muhalli ko daya.
Wallahi garwashin bidarsa du da shi,
Ya k'ona sassan zuciya wayaniya.
Na so ka D'aha kamar ido ga makauniya,
Na so in je ni gare koda sau daya.
Na so ziyara ga ni ba ni da fuffuke,
K'ak'a ni kai in gano masoyin zuciya.
Na so ka san mai wabiya da ta so d'iya,
Koko muridhi yadda ya so lafiya.
Ko son abinci ga wanda ya yunwata,
Koko ruwa ga mai k'ishi da ya sha wuya.
Mukhtaru ka tafi ban ganka a duniya,
Ko na rabauta in ganka ko kun kwanciya.
Acikin mafarkin in na samu sai in ce,
Allahu Akbar u'uhu wayyoniya.
Begenka ya k'onan k'ashi har jijiya,
Naman jikina ya zagwanye bai d'aya.
Ya k'ona hanta har da hanji duka,
Ya bar hawayen zuciya da idaniya.
K'aunarka ta k'one buk'atar zuciya,
Sai ko ganinka da yammaci ko safiya.
Ta ya da zancen duniya tatsuniya
Ta dauki amri wanda ya zam gaskiya.
Ta ya da zancen zo-mu-ji-ta da kan fad'a,
Ta kalmashe gizo ta hana masa k'ok'iya.
Duka zuciyar da ta so ka D'aha da gaskiya,
Wallahi ta arzurta ba shauran tsiya.
Tai sitira ta tufata launi bam da bam,
La budda tai sha'ani irin na hawainiya.
Wata safiya tai murmushi wata safiya,
Riga fara wataran ta sawo shudiya.
Wataran da alkebba fara wataran ko,
Ya fashe da kuka ni a wa d'an saniya.
K'ak'a ni kai na bak'in cikin nan duniya,
Wa zan k'ara gunsa ne wayyo niya.
Ko na yi k'ara babu mai ji ko ya zam,
kukan amale ni ka yi ko jiniya.
Mukhtaru ya faku ga ganinsa yai wuya,
Belle in ce masa D'aha ni na sha wuya.
Shi ne abin k'ara gare shi gani na sa,
Ya zam kamar k'oyin farar hankakiya.
Da na san ganinsa yana da 'yar farkar wuya,
Na dauki jurewa ina ta dawainiya.
Dan babu wanda nake da shi zai taimakan,
Na sauke kayan zuciya sai d'uriya.
Na ce ganin maka abbukatar zuciya,
In dai na sami Wallah ya koran tsiya.
In je ni haifu minan isamguri na je,
In sha ruwan zam-zam inuta in kewaya.
In je safa in je ni marwa indawaya,
In je musallaci in jiranci mazan jiya.
Sannan in dawo in d'awafin sallama,
Bayan muk'amin nan da D'aha ya tsai tsaya.
In yo hajina kamili in masgaya,
Ni dai nufina gun mazajen gaskiya.
Ko da ina yin rarrafe in ja jiki,
In zo madina gurin Habibu abin biya.
In je ni raudhan nan ta D'aha in sunkuya,
In gaisuwa in biya bukatar zuciya.
Dan Anbiya nasa na kira ka rabbana,
Ka jikan masoyan D'aha yamma da safiya.
Ganar dani Mukhtari D'aha alaniya,
Domin ya koran duk jami'u shujuniya,
Dauke hijabi Rabba in gan shi fai,
Nan duniya ya Rabbi ko a manamiya.
Rahmarka ta gama kowanne balle niya,
Dana dauki k'arata ilaika Ilahiya.
Ya Rabbi nai kara gare ka fa kai daya,
Bayanka waye za ya amsa du'a'iya.
Kayyo Salati Rabbi gun mata nasa,
Kayo wata Rabbi gun sahabu da aliya.
Duk sanda mai bege ya ce k'ul safiya,
Sallu Alal Mukhtari koda sau daya.
Auk'ala zuttashd'iri fi takmilihi,
Begen Muhammadu ya cikamin zuciya.
Friday, June 29, 2007
"Na tuba na bi Ubangiji" Wakar Marigayi Malam Nasiru Kabara, Allah ya yi masa rahama, Ameen.
Na tuba na bi Ubangiji,
Na daina aikin munkari.
Na kama turbar Annabi,
Gwadabe mikakke D'ahiri.
Na tabbata da Ubangiji daya ne,
A b'oye da zahiri,
Na kama hanyar shugaban,
Duka sayyadi Abdulk'adiri.
Na jure cutar d'an Adam,
Domin na tabbata ankuri.
Na dena zagin dan Adam,
Balle in ce masa kafiri.
Na tuba ni na bar kula,
Da makangara a cikin gari.
Na dena Sallah ni kad'an,
Na bar k'awar duka ja'iri.
Sallah cikin jama'ar masallaci,
Adan Alamajiri.
Duka wanda ya zage ni,
Kai masa gafara Ya Gafiri.
Zikiri a kowanne lokaci,
Safe da yamma da daddare.
Shi ne abinci na da shi,
Aka sanni du a cikin gari.
Aljanna na hannun iyaye,
Na rok'e su sunadari.
Na roki Jalla Ubangiji,
Ya tsare ni aikin munkari.
Na yo salati da salama,
A gurin Muhammadu D'ahiri.
Ya Rabbi kai mana gafara,
Don sayyadi Abdulkadiri.
Insha Allahu daga lokaci zuwa lokaci zan dinga sako wakokin Malamin, domin su ba zu a ko'ina, a haka ne jama'a za su karu da hikimomin da Allah ya horewa Malamin.
Na daina aikin munkari.
Na kama turbar Annabi,
Gwadabe mikakke D'ahiri.
Na tabbata da Ubangiji daya ne,
A b'oye da zahiri,
Na kama hanyar shugaban,
Duka sayyadi Abdulk'adiri.
Na jure cutar d'an Adam,
Domin na tabbata ankuri.
Na dena zagin dan Adam,
Balle in ce masa kafiri.
Na tuba ni na bar kula,
Da makangara a cikin gari.
Na dena Sallah ni kad'an,
Na bar k'awar duka ja'iri.
Sallah cikin jama'ar masallaci,
Adan Alamajiri.
Duka wanda ya zage ni,
Kai masa gafara Ya Gafiri.
Zikiri a kowanne lokaci,
Safe da yamma da daddare.
Shi ne abinci na da shi,
Aka sanni du a cikin gari.
Aljanna na hannun iyaye,
Na rok'e su sunadari.
Na roki Jalla Ubangiji,
Ya tsare ni aikin munkari.
Na yo salati da salama,
A gurin Muhammadu D'ahiri.
Ya Rabbi kai mana gafara,
Don sayyadi Abdulkadiri.
Insha Allahu daga lokaci zuwa lokaci zan dinga sako wakokin Malamin, domin su ba zu a ko'ina, a haka ne jama'a za su karu da hikimomin da Allah ya horewa Malamin.
Subscribe to:
Posts (Atom)